Home General Kwamitin zaman lafiya ya yi kira da a kwantar da hankula

Kwamitin zaman lafiya ya yi kira da a kwantar da hankula

Kwamitin karkashin Janar Abdulsalami Abubakar ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da kwamitin ya fitar, inda ya ce tun bayan gudanar da zaɓe ranar Asabar sun sanya ido, inda ya ce duk da cewa an samu kura-kurai da ‘yan matsaloli, amma zaɓukan sun gudana lami lafiya.

Wannan kira na kwamitin zaman lafiya na zuwa ne bayan da manyan jam’iyyun adawa a zaben shugaban Najeriya ke kokawa kan ingancin sa.

Ya ce a daidai lokacin da hankali ya karkata wajen jin sakamakon zaɓen, suna kira ga hukumar zaɓe da ta saurari korafe-korafen mutane wajen gudanar da bincike kan zargin tafka maguɗi da tabbatar da an yi wa dukkan waɗanda suka fita suka yi zaɓe adalci.

Kwamitin ya ce ya samu rahotannin da suka nuna cewa an musguna wa wasu masu zaɓe a sassan ƙasar da dama ta hanyar tayar da rikici da hargitsa wajen kaɗa kuri’a da sayen kuri’a da kuma matsalolin da aka fuskanta da na’urar tantance masu zabe.

Tsohon shugaban ƙasar ya ce yana kira ga dukkan ‘yan takarar shugaban ƙasa da cewa su ne za su ɗauki alhakin duk abin da masu magana da su suka faɗa, inda ya ce su guji furta kalaman da za su tayar da rikici ganin cewa sun rattaɓa hannu kan yarjejeniyar yin zaɓe lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp