Home General Buhari ya jajantawa wadanda gobara ta kone dukiyar su a Jihar Legas

Buhari ya jajantawa wadanda gobara ta kone dukiyar su a Jihar Legas

Shugaba Muhammadu Buhari ya jajanta wa waɗanda gobara ta kona wa shaguna a kasuwa sayar da kayan mota da ke jihar Legas a kudancin Nijeriya.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin yaɗa labarai ga shugaban Malam Garba Shehu ya fitar, ta ce shugaban ya nuna alhini kan abin da ya faru da ‘yan kasuwar da kuma iyalansu, inda ya nuna takaici kan irin asarar dukiya ta miliyoyin naira da aka yi a kasuwar.

Ya yi kira ga hukumomi a jihar da su tabbatar sun ɗauki matakin kare afkuwar hakan nan gaba, inda ya godewa hukumar kashe gobara ta jihar saboda kai agajin gaggawa lokacin da lamarin ya faru.

Buhari ya kuma miƙa ta’aziyya ga iyalan wani mai gadi mai shekara 65 da ya rasu a sanadiyyar gobarar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp