Buhari ya jajantawa wadanda gobara ta kone dukiyar su a Jihar Legas

Shugaba Muhammadu Buhari ya jajanta wa waɗanda gobara ta kona wa shaguna a kasuwa sayar da kayan mota da ke jihar Legas a kudancin Nijeriya.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin yaɗa labarai ga shugaban Malam Garba Shehu ya fitar, ta ce shugaban ya nuna alhini kan abin da ya faru da ‘yan kasuwar da kuma iyalansu, inda ya nuna takaici kan irin asarar dukiya ta miliyoyin naira da aka yi a kasuwar.

Ya yi kira ga hukumomi a jihar da su tabbatar sun ɗauki matakin kare afkuwar hakan nan gaba, inda ya godewa hukumar kashe gobara ta jihar saboda kai agajin gaggawa lokacin da lamarin ya faru.

Buhari ya kuma miƙa ta’aziyya ga iyalan wani mai gadi mai shekara 65 da ya rasu a sanadiyyar gobarar.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 21 minutes 26 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 2 minutes 51 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com