Jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi sun sanya hannu a dokar zaman lafiya

‘Yan takarar gwamna na jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi dake arewa maso gabashin Nijeriya sun sanya hannun a yarjejeniyar zaman lafiya gabanin zaben gwamnoni dake tafe ranar asabar a jihohin kasar.

Taron sanya hannun ya gudana ne a ranar laraba a dakin taro na shalkwatar rundunar ‘yan sanda dake jihar Bauchi.

‘yan takarar da suka sami halartar taron sanya hannun sun hadar da gwamnan jihar dake neman wa’adi na 2 a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, sai halliru Dauda Jika, na jam’iyyar NNPP, sai kuma sadique Abubakar na jam’iyyar APC wanda abokin takarar sa Shehu Musa ya wakilce shi a yayin taron.

Sauran sun hadar da ‘yan takarar jam’iyyun LP, YPP, ZLP da kuma PRP, sai dai  a yayin taron ba’a wakilcin jam’iyyun ADC, AC ba.

Haka kuma an hangi wakilcin rundunar sojin Nijeriya, rundunar tsaro ta DSS, jami’an tsaro na Civil Defence, dakarun hukumar hana fasa Kwauri ta Customs, jami’an NDLEA, jami’an dake lura da shige da fice na NIS, da masu lura da ajiya da gyaran hali da tarbiyya.

Kwamishin ‘yan sanda jihar ya karanta sashe na 125 da na 126 na dokar zabe ta 2022 da aka yiwa gyaran fuska matsayin wukar kugun da yayi amfani da ita wajen gargadin ‘yan takarar domin bin doka da Oda a yayin zaben.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 10 minutes 2 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 51 minutes 27 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com