Wani sabon hari a Jamhuriyyar damukradiyya congo yayi sandiyyar mutuwar mutane 40

Wani sabon harin mayakan tayar da kayar baya na ADF a gabashin jamhuriyyar damukradiyyar Congo yayi sanadiyyar mutuwar mutane 40 kamar yadda hukumomi suka bayyana.

Shugaban wata kungiyar Al’umma a kauyen mukondi ne ya tabbata da faruwar lamarin inda yace  mayakan sun hallaka mutanen ne da wukake.

Kungiyar ‘yan tawayen ADF ta samo asali ne daga kasar Uganda wadda ta fara gudanar da ayyukan ta a gabashin Congo a tsakiyar shekarun 1990, wanda aka ce mafi yawa cikin ‘ya’yan kungiyar musulmai ne dake kisan gilla ga fararen hula.

A  shekara 2021 ma an alakanta hare-hare da aka kai kasar Uganda kuma aka kaddamar da wani farmaki na hadin gwiwa tsakanin sojojin congo da na Uganda domin farautar mayakan a Arewacin Kivu da kuma lardin Ituri dake makwabtaka da su.

Ko a makon daya gaba ta kasar Amurka ta sanya tukuicin dala miliyan biyar ga wanda ya bayar da bayanan yadda za’a kama shuganban kungiyar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 34 minutes 1 second,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 15 minutes 26 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com