Home DUNIYA Gwamnatin sojin kasar Mali ta dage Shirin yiwa kundin tsarin mulkin...

Gwamnatin sojin kasar Mali ta dage Shirin yiwa kundin tsarin mulkin kasar gyaran fuska

Gwamnatin sojin kasar Mali ta sanar da dage Shirin yiwa kundin tsarin mulkin kasar gyaran fuska da aka tsara gudanarwa a ranar 19 ga watan Maris din da muke ciki, yayin da ta kara jaddada alkawarin da ta yin a mika Mulki hannun farar hula a shekarar 2024.

Gwamnatin ta sanar da wannan hukunci ne ta hanyar kafa nada wakilai daga hukumar zabe a dukkanin shiyyoyin kasar, da nufin yada sabon kundin tsarin mulkin kasar sassan kasar domin su kai hannun al’umma kai tsaye.

Samar da kundin tsarin Mulki a wannan lokaci dais hi ne zai baiwa sojojin dake Mulkin kasar dake fama da ayyukan masu ikirarin jihadi, damar cigaba da jan ragamar shugabancin kasar har zuwa shekarar 2024 kamar yadda suka alkawarta.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp