Gwamnatin sojin kasar Mali ta dage Shirin yiwa kundin tsarin mulkin kasar gyaran fuska

Gwamnatin sojin kasar Mali ta sanar da dage Shirin yiwa kundin tsarin mulkin kasar gyaran fuska da aka tsara gudanarwa a ranar 19 ga watan Maris din da muke ciki, yayin da ta kara jaddada alkawarin da ta yin a mika Mulki hannun farar hula a shekarar 2024.

Gwamnatin ta sanar da wannan hukunci ne ta hanyar kafa nada wakilai daga hukumar zabe a dukkanin shiyyoyin kasar, da nufin yada sabon kundin tsarin mulkin kasar sassan kasar domin su kai hannun al’umma kai tsaye.

Samar da kundin tsarin Mulki a wannan lokaci dais hi ne zai baiwa sojojin dake Mulkin kasar dake fama da ayyukan masu ikirarin jihadi, damar cigaba da jan ragamar shugabancin kasar har zuwa shekarar 2024 kamar yadda suka alkawarta.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 21 minutes 11 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 2 minutes 36 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com