Home DUNIYA Mata masu juna biyu sama da 80,000 ke mutuwa duk shekara a...

Mata masu juna biyu sama da 80,000 ke mutuwa duk shekara a Najeriya – UNICEF

Wannan na zuwa ne, yayin da hukumomin lafiya na duniya ke ci gaba da jan hankalin kasashe, musamman masu tasowa muhimmancin inganta shirin kula da lafiyar mata masu juna biyu.

Majalisar Duniya ta ce rayuwar mata masu juna biyu, ko kuma yayin haihuwa na cikin matukar hadarin gaske a nahiyar Afirka, don haka ana bukatar samar da wani shiri na musamman da zai magance wannan matsala.

A cewar UNICEF, mata 225 ne ke mutuwa a kowace rana a Najeriya, sakamakon mace-macen mata masu juna biyu ko kuma yayin haihuwa, inda suke neman hukumomi su dauki matakin gaggawa don dakile wannan matsala.

Masana kiwon lafiya na danganta mace-macen mata masu juna biyu ko kuma yayin haihuwa na da nasaba ne da sakaci zuwa duba lafiyarsu a lokacin da ya dace, yayin da wasu kuma ke fama da rashin cibiyoyin kula da lafiya a yankunan su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp