Home DUNIYA Akwai yiwuwar kotun ICC ta yi amfani da Afrika ta kudu wajen...

Akwai yiwuwar kotun ICC ta yi amfani da Afrika ta kudu wajen kame Putin

Hankulan duniya sun karkata kan Afrika ta Kudu kasar da ake ganin kotun Duniya ta ICC na shirin amfani da ita wajen kame shugaba Vladimir Putin na Rasha wanda kotun ta fitar da takardar sammacin kamen shi a ranar 17 ga watan Maris din da muka yi bakwana da shi.

Alamomi na nuni da cewa ita kanta gwamnatin shugaba Cyril Ramaphosa na halin tsaka mai wuya lura da yadda jagoran na Moscow ke Shirin ziyartar kasar a watan Agusta mai zuwa don halartar taron kungiyar BRICS.

Karkashin dokokin kotun hukuntan manyan laifukan ta ICC wadda Afrika ta kudu ke matsayin mamba a cikinta, wajibi ne kasar ta mika duk wani da kotun ke nema da zarar ya sanya kafa a Pretoria, lamarin da ke matsayin babbar damuwa ga ziyarar ta Putin.

Tun zamanin mulkin Nelson Mandela a shekarun 1988 Afrika ta kudu ke karkashin kotun ta Duniya tare da mutunta hukunce-hukuncenta, sai dai ana ganin abu ne mai wuya kasar ta amince da zama sanadin mika Putin lura da alakar Rasha da kasar.

Ministan da ke kula da alakar kasar da ketare, Naledi Pandor ya shaidawa manema labarai cewa yanzu haka suna tattaunawa don samun haske kan yadda za su tunkari wannan matsala.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp