Home General Tun bayan yaƙin basasa, Najeriya bata ta ba fuskantar rarrabuwar kawuna kamar...

Tun bayan yaƙin basasa, Najeriya bata ta ba fuskantar rarrabuwar kawuna kamar yanzu ba – Sanusi Lamido Sunusi

Khalifan Tijjaniyya, Muhammadu Sanusi II ya yi gargaɗi cewa Najeriya ta fi fama da rarrabuwar kai saboda ƙabilanci da bambancin addini tun bayan yaƙin Biafra fiye da shekara 50 da ta wuce.

Da yake jawabi a wani taro a Legas, Muhammadu Sanusi wanda ya ce “ba na tunanin Najeriya ta taɓa kasancewa a mawuyacin yanayi kamar yanzu tun bayan yaƙin basasa. Muna da ƙalubale game da aikin gina ƙasar nan.

Ya ce Najeriya tana fama da bambance-bambancen addini da na ƙabilanci.

“Muna da tattalin arzikin da ke fuskantar taɓarɓarewa kuma abin takaici, da alama muna fama da ƙarancin shugabanci na gari.”

Kalaman tsohon gwamnan CBN ɗin na zuwa ne yayin da Shugaba Muhammadu Buhari ke shirye-shiryen miƙa mulki ga Bola Tinubu.

Tinubu ne ya yi nasara a kan manyan abokan takararsa – Atiku Abubakar da Peter Obi a zaɓen shugaban ƙasar mai zafi da aka yi a watan Fabrairu.

Atiku da Obi sun yi fatali da sakamakon zaɓen, kuma tuni suka shigar da ƙara a kotu

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp