Home DUNIYA Adadin mutanen da aka kashe a rikicin Sudan ya kusan 100

Adadin mutanen da aka kashe a rikicin Sudan ya kusan 100

Kungiyar likitoci a Sudan, ta ce adadin wadanda aka kashe a fadan da ake cigaba da gwabzawa tsakanin sojojin kasar da jami’an tsaron rundunar musamman ta kai daukin gaggawa wato ‘Rapid Response’, ya karu zuwa mutane 97, cikinsu kuwa har da jami’an majalisar dinkin duniya uku.

Tun a ranar Asabar, rikicin ya barke bayan da aka kwashe makwanni ana takaddama tsakanin hafsan sojin Sudan Abdel Fattah al-Burhan da mataimakinsa Mohamed Hamdan Daglo, wanda ke jagorantar rundunar dakarun RSF mai karfin fada a ji, wadda shugaba Burhan ke son narkar da ita zuwa cikin rundunar sojin kasar.

Kazamin fadan ya cigaba da yin kamari ne kuma duk da cewar bangarorin biyu sun cimma yarjejeniyar tsagaitar wutar wucin gadi a ranar Lahadi, domin ba da damar bai wa wadanda rikicin ya rutsa da su kulawar gaggawa.

Likitoci sun ce daruruwan mutane ne suka jikkata, yayin da hukumar lafiya ta duniya WHO ta yi gargadin cewa kusan dukkanin asibitoci 9 da ke birnin Khartoum, basu da jini da kuma ruwa da marasa lafiya ke bukata.

A halin da ake ciki hukumar samar da abinci ta majalisar dinkin duniya WFP da aka kashewa jami’ai uku, ta dakatar da ayyukanta a Sudan har sai abinda hali yayi.

Tuni dai kasashe da dama suka yi Allah wadai da gumurzun da ake yi tsakanin sojojin gwamnati da dakarun musamman na RSF, yayin da wasu kasashen kamar Chadi da Masar suka rufe iyakokinsu da kasar ta Sudan.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken da takwaransa na Birtaniya James Cleverly, sun bayyana matukar damuwa game da kazamin fadan da suka bayyana a matsayin barazana ga makwaftan Sudan ba ma al’ummar kasar kadai ba.

Yau Litinin ake sa ran shugaban kungiyar Tarayyar Afirka AU, Moussa Faki Mahamat, zai isa kasar domin shiga tsakani da jagorantar kulla yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp