Home DUNIYA An amince da yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta ta sa’a 24 a Sudan...

An amince da yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta ta sa’a 24 a Sudan – RSF

Dakaru masu sanye da kayan sarki na RSF da ke faɗa da sojojin Sudan sun bayyana amincewa da yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta ta sa’a 24, fara wa da misalin karfe 6 na yamma.

Cikin wata sanarwa da dakarun suka wallafa a shafinta na Twitter, ta ce “Mun amince da kudurin tsagaita buɗe wuta, kuma muna fatan sauran ɓangarorin za su bi yarjejeniyar da aka cimma,” in ji kungiyar

Sai dai babu tabbacin cewa ko sojojin Sudan sun amince da tsagaita buɗe wutan.

Ɓangarorin biyu sun ce za su mutunta yarjejeniyar tsagaita wuta ta sa’o’i 24 a ranar Talata.

Ana dai ci gaba da gwabza kazamin faɗa a ƙasar ta Sudan, musamman a kusa da hedkwatar sojojin da ke tsakiyar birnin Khartoum.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp