Home DUNIYA Janar-Janar da ke rikicin Sudan sun amince su tsagaita wuta ta tsohon...

Janar-Janar da ke rikicin Sudan sun amince su tsagaita wuta ta tsohon kanaki 3 – Blinken

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya ce janar-janar da ke rikici a Sudan sun amince sun tsagaita wuta ta kwana uku ranar Litinin, bayan an kwashe kwana 10 ana fafatawa tsakaninsu.

Yarjejeniyoyin tsagaita wutar da suka kulla a baya ba su yi tasiri ba lamarin da ya kai ga kisan daruruwan mutane da kuma raba dubbai daga gidajensu.

Sai dai Blinken ya ce “bayan an kwashe sama da awa 48 ana tattaunawa sosai, Rundunar Sojin Sudan da Rapid Support Forces (RSF) sun amince su aiwatar da jarjejeniyar tsagaita wuta ta awa 72 daga ranar Litinin da daddare.”

Sakataren Wajen Amurka ya yi kalaman ne awa biyu kafin a soma aiwatar da yarjejeniyar.

Hakan na faruwa ne a lokacin da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadin cewa Sudan na “dab da fadawa cikin bala’i” sakamakon rikici tsakanin bangarorin biyu, wadanda ke fafatawa a Khartoum da wasu bangarori na kasar.

An kashe akalla mutum 427 yayin da fiye da mutum 3,700 suka jikkata sakamakon rikicin, a cewar hukumomin Majalisar Dinkin Duniya.

Wani babban jami’in ofishin jakadancin Masar a Khartoum yana cikin wadanda aka kashe a baya bayan nan, a cewar ma’aikatar wajen kasar.

An kashe shi ne yayin da yake kan hanyar zuwa ofishin jakadancin domin sanin halin da ake ciki game da yiwuwar kwashe su daga Sudan.

Rikicin na faruwa ne tsakanin runsunar sojin da ke karkashin Janar Abdel Fattah al Burhan da dakarun RSF da ke karkashin tsohon mataimakinsa Janar Mohamed Hamdan Dagalo.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp