Home DUNIYA Rikicin Sudan ka iya zamar wa duniya ƙarfe-ƙafa – Abdallah Hamdok

Rikicin Sudan ka iya zamar wa duniya ƙarfe-ƙafa – Abdallah Hamdok

Tsohon Firaministan Sudan Abdallah Hamdok ya yi gargaɗin cewa rashin tsaron da ƙasar ke fuskanta zai iya zarta na Siriya da Libya.

Mista Hamdok na wannan maganar ne yayin da ake ci gaba da samun rahotonnin kai farmaki da jiragen sama a kan wuraren da ke hannun dakarun RSF a birnin Khartoum.

Duk ɓangarori biyun da ke yaƙi da juna na zargin juna da karya yarjejeniyar tsagaita wuta. Dubban mutane ne suka fice daga gidajensu sakamakon yaƙin.

Tsohon Firamistan ya bayyana yaƙin da rashin hankali tare da cewa yaƙi ne da babu wanda zai yi nasara a cikinsa, sai dai hasarar rayuka masu yawa da zai haifar.

Ya ce akwai buƙatar ƙasashen duniya su yi aiki tare domin zaunar da shugabanin rundunonin da ke yaƙi da juna a ƙasar da jagoran dakarun RSF a teburiun sulhu domin kawo ƙarshen yaƙin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp