MDD zata cigaba da kai agaji a kasar Sudan

Hukumar Abinci ta majalisar Dinkin Duniya ta ce za ta maido da ayyukanta a Sudan yayin da yaƙi a ƙasar ke yi wa miliyoyin mutane barazanar faɗawa ƙangin yunwa.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin hukumar ta ce tana sa ran fara rabar da abinci a jihohin Gedaref da Gezira da Kassala da kuma jihar White Nile a cikin kwanaki masu zuwa.

“Za mu ɗauki matakai domin tabbatar da kare lafiyar ma’aikatanmu da ƙawayenmu yayin da muƙe ƙoƙarin taimaka miliyoyin mutane da ke cikin tsananin buƙatar taimakon”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Hukumar ta dakatar da ayyukanta a ƙasar ne tun a ranar farko da aka fara yaƙin bayan da aka kashe ma’aikatanta uku.

Hukumar Abincin ta Majalisar Dinkin Duniyar ta bayyana cewa mutum miliyan 15 na cikin tsananin buƙatar abinci da rashin tsaro, tun kafin ɓarkewar rikicin.

Ta kuma bayyana cewa adadin zai ƙara yayin da ake ci gaba da faɗan.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 15 hours 29 minutes 41 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 17 hours 11 minutes 6 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com