Home DUNIYA Sama da mutane dubu 800 za su gudu daga Sudan- MDD

Sama da mutane dubu 800 za su gudu daga Sudan- MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta ce sama da mutane dubu 800 ne ake sa ran za su tsere daga Sudan sakamakon kazamin rikicin da ake yi tsakanin rundunar sojin kasar da dakarun Kai Daukin Gaggawa na RSF.

Wani babban jami’in Majalisar Dinkin Duniya, Raouf Mazou ne ya bayyana haka a Geneva, ina yake cewa idan ba a warware wannan rikici da wuri ba, za a ci gaba da samun dimbim mutanen da ke arcewa daga Sudan don neman mafaka da agaji.

Saboda haka ya ce a tattaunawar da suka yi da hukumomin da wannan lamari zai shafa, sun cimma matsayar shirya wa mutane dubu 815 da ake sa ran za su iya arcewa zuwa kasashe 7 da ke makwaftaka da Sudan.

Wannan hasashe da aka yi, in ji Mazou ya hada da kimanin ‘yan kasar Sudan dubu 580 da kuma wadanda ke gudun hijira a halin yanzu daga Sudan ta Kudu da wasu wuraren.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp