Home DUNIYA ECOWAS na shirin Lashe amai kan Jamhuriyar Nijar

ECOWAS na shirin Lashe amai kan Jamhuriyar Nijar

Alamu na nuna cewa kungiyar ECOWAS na shirin janye barazanar amfani da karfin soji domin mayar da zababiyar gwamnatin a Jamhuriyar Nijar.

Wannan na zuwa ne bayan wata ganawa da kungiyar da mambobinta a birnin tarayyar Nijeriya aa batun juyin mulkin kasar.

A yayin taron kungiyar Kasashen Afrika ta Yamma, ta ce za ta ci gaba tintibar sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar a yunkurin da take na warware matsalar.

Yayin bude taro na musammman da shugabannin kungiyar a Abuja, shugaban ECOWAS Bola Ahmed Tinubu da ke jagorancin taron ya bayyana taron na yau a matsayin mai matukar muhimmanci wajen ci gaba da dorewar yankin a matsayin dunkulalle wanda zai ta taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da kuma ci gaban Al’umma.

Shugaban ya ce taronsu na yau zai bada damar cikakken nazari kan ci gaban da aka samu da kuma matsalolin da aka fuskanta tun bayan taron farko da suka yi kan Nijar, domin duba gyaran da ya kamata a yi ko kuma gibin da ya kamata a cike domin gyara lamarin.

Shugaban na ECOWAS ya ce ya zama wajibi a gare su a matsayin shugabanni su fahimci cewar halin da ake ciki a Nijar na zama barazana a gare su, kuma abin da ke iya biyo baya zai shafi yankin baki daya.

Tinubu ya bayyana fatar cewar wannan taro na biyu kan Nijar zai bada damar daukar matakin da ya dace wanda zai taimaka wa yankin baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp