Home DUNIYA Burkina Faso za ta aika wa Nijar kayan abinci

Burkina Faso za ta aika wa Nijar kayan abinci

Wasu rahotanni na bayyana cewa Gwamnatin Burkina Faso na shirin aika wa da maƙwabciyarta Nijar hatsi.

Wata sanarwa da ma’aikatar cigaban kasuwanci ta ƙasar ta fitar ranar Juma’a ta ce za a aika wa Nijar ɗin gero da masara da dawa, da dai sauransu.

Yunƙurin na zuwa ne yayin da ƙungiyar ECOWAS  ta ƙaƙaba wa Nijar takunkuman kasuwanci da na tattalin arziki sakamakon juyin mulkin da ya kifar da gwamnatin Shugaba Mohamed Bazoum a ƙarshen watan Yuli.

Duk da cewa Burkina Faso mamba ce a ECOWAS, ba ta bi umarnin ƙungiyar ba ta raya tattalin arziƙin Afirka ta Yamma saboda ita ma tana cikin takunkumai na juyin mulki.

Sanarwar ta kuma yi kira ga ‘yan kasuwar da ke da sha’awar safarar kayan su tuntuɓi hukumomin da suka dace don isar da kayan zuwa Nijar.

Burkina Faso, da Mali, da Guinea dukkansu mambobin Ecowas da aka dakatar saboda juyin mulki, sun sanar da cewa za su goya wa sojojin mulkin Nijar baya idan ƙungiyar ko kuma dakarun ƙasar waje suka kai musu hari.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp