Home DUNIYA Burkina Faso za ta aika wa Nijar kayan abinci

Burkina Faso za ta aika wa Nijar kayan abinci

Wasu rahotanni na bayyana cewa Gwamnatin Burkina Faso na shirin aika wa da maƙwabciyarta Nijar hatsi.

Wata sanarwa da ma’aikatar cigaban kasuwanci ta ƙasar ta fitar ranar Juma’a ta ce za a aika wa Nijar ɗin gero da masara da dawa, da dai sauransu.

Yunƙurin na zuwa ne yayin da ƙungiyar ECOWAS  ta ƙaƙaba wa Nijar takunkuman kasuwanci da na tattalin arziki sakamakon juyin mulkin da ya kifar da gwamnatin Shugaba Mohamed Bazoum a ƙarshen watan Yuli.

Duk da cewa Burkina Faso mamba ce a ECOWAS, ba ta bi umarnin ƙungiyar ba ta raya tattalin arziƙin Afirka ta Yamma saboda ita ma tana cikin takunkumai na juyin mulki.

Sanarwar ta kuma yi kira ga ‘yan kasuwar da ke da sha’awar safarar kayan su tuntuɓi hukumomin da suka dace don isar da kayan zuwa Nijar.

Burkina Faso, da Mali, da Guinea dukkansu mambobin Ecowas da aka dakatar saboda juyin mulki, sun sanar da cewa za su goya wa sojojin mulkin Nijar baya idan ƙungiyar ko kuma dakarun ƙasar waje suka kai musu hari.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp