Gwamnatin Tarayya ba za ta yi katsalandan a zaben Bayelsa, Imo da Kogi ba

Gwamnatin Nijeriya tace ba za ta yi katsalandan a zaɓukan jihohin Bayelsa da Kogi da kuma Imo ba, da ke tafe cikin watan Nuwamba.

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin wani taro da shugaban hukumar zaɓen ƙasar, Farfesa Mahmood Yakubu, tare da sauran kwamishinonin zaɓen da sauran masu ruwa da tsaki a sabgar zaɓen.

Ya ce shugaban ƙasar Bola Tinubu na cike da fatan gudanar da sahihin zaɓe a waɗannan jihohi.

“Wannan zaɓuka za su kasance mafiya tsafta fiye da na baya. za su gudana ba tare da rigima ba, za su kasance sahihan zaɓukan da babu katsalandan a cikinsu,” in ji Ribadu.

Ya kuma ce shugaban ƙasa a shirye yake ya goyi bayan hukumar don samun nasarar hakan.

An gudanar da taron ne a ofishinsa a wani ɓangare na tuntuɓa da hukumar ke yi gabanin zaɓukan da ke tafe ranar 11 ga watan Nuwamba.

Tun da farko INEC ta nuna fargabar tsaro gabanin zaɓukan, a wani taro da ta gudanar da jam’iyyun siyasa.

A nasa ɓangare shugaban INEC, ya bayyana fargabarsa kan tsaron lafiyar masu kaɗa ƙuri’a da tsaron kayayyakin zaɓe masu muhimmanci, tare da tsaron cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe.

Ya yi kira ga jami’an tsaro su yi maganin duk wanda ya yi yunƙurin tayar da zaune-tsaye a ranar zaɓen.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 39 minutes 41 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 21 minutes 6 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com