‘Yan Sanda Sun tabbatar da harin ‘yan Ta’adda a jihar Adamawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta tabbatar da harin ‘yan bindiga a garin Kwapre dake karamar hukumar Hong ta jihar.

kakakin rundunar ‘yan sandan jihar SP Sulaiman Ngureje ne ya bayyana hakan ga manema labarai ranar talata a birnin Yola.

inda ya ce lamarin ya auku ne ranar litinin, wato ranar da aka gudanar da bikin kirsimeti, sai dai ya ce har yanzu hukumar na gudanar da bincike bisa aukuwar lamarin.

 ya kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar Babatola Afolabi, ya bayar da umarnin girke jami’an ‘yan sanda domin gudanar da bincike.

ya kuma bukaci al’umma da su tabbatar sun kai rahoton dukkan wani abu da basu yadda da shi ba ga hukumar da kuma dukkan saurarn hukumomin tsaro dake jihar dama kasa baki daya.

haka shima dagacin Dugwaba Mr Simon Buba,  ya tabbatar da faruwar lamarin, in da yace maharan sun hallaka mutane 2,

ya ce ana zargin maharan mambobin kungiyar tayar da kayar baya na  boko haram ne, da suka yiwa garin tsinke kan babura suka kuma yi awon gaba da kayan abinci suka nausa cikin dajin sambisa.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 13 minutes 12 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 54 minutes 37 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com