Home General ‘Yan Sanda Sun tabbatar da harin ‘yan Ta’adda a jihar Adamawa

‘Yan Sanda Sun tabbatar da harin ‘yan Ta’adda a jihar Adamawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta tabbatar da harin ‘yan bindiga a garin Kwapre dake karamar hukumar Hong ta jihar.

kakakin rundunar ‘yan sandan jihar SP Sulaiman Ngureje ne ya bayyana hakan ga manema labarai ranar talata a birnin Yola.

inda ya ce lamarin ya auku ne ranar litinin, wato ranar da aka gudanar da bikin kirsimeti, sai dai ya ce har yanzu hukumar na gudanar da bincike bisa aukuwar lamarin.

 ya kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar Babatola Afolabi, ya bayar da umarnin girke jami’an ‘yan sanda domin gudanar da bincike.

ya kuma bukaci al’umma da su tabbatar sun kai rahoton dukkan wani abu da basu yadda da shi ba ga hukumar da kuma dukkan saurarn hukumomin tsaro dake jihar dama kasa baki daya.

haka shima dagacin Dugwaba Mr Simon Buba,  ya tabbatar da faruwar lamarin, in da yace maharan sun hallaka mutane 2,

ya ce ana zargin maharan mambobin kungiyar tayar da kayar baya na  boko haram ne, da suka yiwa garin tsinke kan babura suka kuma yi awon gaba da kayan abinci suka nausa cikin dajin sambisa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp