Home DUNIYA An dakatar da kafafen yaɗa labaran BBC da VOA a Burkina Faso

An dakatar da kafafen yaɗa labaran BBC da VOA a Burkina Faso

Hukumar da ke sa ido kan kafafen yaɗa labarai a Burkina Faso ta ƙaƙaba dakatarwar mako biyu kan kafar yaɗa labarai na BBC Afrique da Muryar Amurka (VOA) saboda yaɗa rahoton da ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Human Rights Watch ta fitar da ke zargin sojojin ƙasar da cin zarafin farar hula.

Kazalila, hukumar ta dakatar da shafukan intanet na kafofin yaɗa labaran da ƙungiyar Human Rights a cikin ƙasar.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasar ya ruwaito cewa “An umarci BBC da VOA ta hannun wakilansu a Burkina Faso da su gaggauta daina watsa shirye-shirye a dukkanin kafofinsu,”

Hukumar kula da harkokin sadarwa ta sake gargaɗin kafafen yaɗa labarai a ƙasar da su kaucewa yaɗa labarin inda ta yi barazanar ƙaƙaba wa waɗanda suka bijire takunkumi.

A ranar Alhamis ne ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Human Rights Watch ta zargi sojojin Burkina Faso da kashe farar hula aƙalla 223 a arewacin ƙasar ranar 25 ga watan Fabarairu.

A Disamban 2023 ne Burkina Faso ta dakatar da jaridar French daily Le Monde kan zargin nuna son kai a rahotannin da suke yaɗawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp