An sake dawo da ƙoƙarin bin hanyar diflomasiya domin kawo ƙarshen yaƙin Gaza, inda ake sa rai wakilai daga Hamas za su ci gaba da tattaunawa a birnin Alƙahira na Masar.
An rawaito wani babban kwamandan Hamas na cewa basu da matsala da sabon daftarin yarjejeniyar da Isra’ila ta gabatar kan tsagaita wuta da sakin fursunoni.
Sai dai babu alamar da ke nuna za a cimma daidaituwar.
Read Also:
Rahotanni na cewa sabbin bayanan yarjejeniyar sun ƙunshi dawo da kwanciyar hankali a Gaza, wanda tabbas za su dadaɗa wa Hamas.
Mataimakin kakakin majalisar Isra’ila Moshe Tur- Paz, ya nuna cewa abin da ya kamata a fi bai wa fifiko a yanzu shi ne dawo da mutanensu da ke garƙame gida.
Sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken ya je Saudiyya, inda shi ma yake tattaunawa da shugabannin Larabawa kan yiwuwar cimma yarjejeniya.
PRNigeria hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 18 hours 42 minutes 24 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 23 minutes 49 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com