Home DUNIYA Mutum 44 sun kamu da cutar kwalara a Kenya sakamakon ambaliyar ruwa

Mutum 44 sun kamu da cutar kwalara a Kenya sakamakon ambaliyar ruwa

An samu rahoton mutum 44 sun kamu da cutar kwalara a lardin Tana River da ke Kenya yayin da ambaliyar ruwa ke ƙara buɗe ƙofar yaɗuwar cututtukan da ake iya ɗauka ta ruwa.

Sanarwa da Hukumar lafiya ta duniya ta fitar wadda ta bayyana adadin, inda ta ce hukumomi a Kenya tare da goyon bayan WHO da kuma sauran hukumomi na sa ido a kan cutar da matakan da za a ɗauka a faɗin ƙasar yayin da ake fama da ambaliyar.

Ambaliyar ta shafi kashi ɗaya cikin huɗu na mutane miliyan ɗaya tare da samun rahoton mutuwar mutum 238 a faɗin ƙasar. Tana River na ɗaya daga cikin lardunan da ambaliyar ta fi shafa a Kenya.

A ranar Talata ne babbar sakatariyar lafiya ta Kenya Mary Muthoni ta ce akwai babbar barazana na yiwuwar cututtukan da ke yaɗuwa ta ruwa su zama annoba idan ba a ɗauki mataki da wuri ba.

Ms Muthoni ta yi magana ne yayin da ita da sauran jami’an lafiya suke raba kayayyakin tsabtace ruwa a babban birnin Nairobi.

Ta kuma yi magana a kan haɗarin cututtukan da ake samu a lalataccen abinci da abincin da aka samu daga hanyoyi marasa nagarta da ambaliyar ta janyo ƙaruwarsu.

WHO ta ce za ta ci gaba da ba da goyon baya ga matakan gaggawa na gwamnati kuma za ta “ci gaba da sa ido kan ɓarkewar cututtuka da ka iya saurin yaɗuwa idan ba a yi saurin magance su ba”.

Ta kuma ce, “WHO ta kuma samar da kayayyakin magance cutar ta kwalara da ake rarrabawa a muhimman larduna wanda za su iya warkar da mutum 10,000”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp