Home General Ambaliyar ruwa ta raba dubbai da muhallinsu a jihar Sokoto – NEMA

Ambaliyar ruwa ta raba dubbai da muhallinsu a jihar Sokoto – NEMA

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta ce ambaliyar ruwa ta raba dubban mutane da muhallansu a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin ƙasar.

wannan na cikin wata sanarwa da hukumar ta NEMA ta wallafa a shafinta na X, in da ta ce ambaliyar da ta faru ranar Litinin ta shafi garuruwa kusan 20 a ƙananan hukumomin Shagari da Tureta.

“Ruwan ya shafe gadar da ke haɗa Shagari da Tureta baki ɗaya kuma ya hana mutane zirga-zirga a yankin,” a cewar sanarwar.

“Haka nan ambaliyar ta shafi ayyukan noma, inda ta shafe gonaki da dama.”

ko dai a ‘yan tsakanin nan Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet), ta yi gargaɗin samun ambaliyar a wasu jihohin ƙasar sakamakon mamakon ruwan sama da za a samu kwanan nan.

Hukumar ta ce jihohin da suka haɗa da Kano, da Katsina, da Zamfara, da Jigawa da Kebbi da Kaduna, da kuma jihar Adamawa na cikin barazanar fuskantar ambaliyar ruwa.

ko da yake dai hukumar bata ambaci jihar Sokoto a cikin jerin jihohin da zasu iya samun ambaliyar ba, ko da yake ta bukaci suaran al’umma dasu dauki matakin da suka dace wajen gyara magunan ruwan su tare da kaucewa yin gini akan hanyar ruwa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp