Home General Gwamnan Jihar Sokoto ya magantu kan kisan sarkin Gobir

Gwamnan Jihar Sokoto ya magantu kan kisan sarkin Gobir

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu ya miƙa ta’aziyarsa a kan rasuwar Hakimin Gatawa Alhaji Isa Muhammed Bawa, wanda ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane.

A saƙon jajen, gwamnan ya ce yana miƙa saƙon jajensa zuwa ga iyalan marigayin da mutanen Sabon Birni da dukkan mutanen jihar.

Cikin wata sanarwa da Sakataren Watsa Labaransa, Abubakar Bawa ya fitar, Aliyu ya ce gwamnatinsa ba za ta huta ba har sai an kawo ƙarshen ayyukan ƴan bindiga a jihar.

Gwamna Aliyu ya bayyana kisan a matsayin “rashin tausayi da dabbanci”, wanda dole a yi Allah-wadai da shi.

Sanarwar ta bayyana mamacin a matsayin mai gaskiya da amana, da son zaman lafiya wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen aiki ga al’umma.

Dokta Aliyu ya yi kira ga jami’an tsaro a jihar da su ƙara ƙoƙari a kan wanda suke yi domin tabbatar da tsaro a jihar, sannan su yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa an kama waɗanda suka kashe hakimin domin su fuskanci hukunci.

Tuni dai Al’ummar garin Sabon Birni a jihar suka gudanar da sallar janazar Sarkin Gobir na Gatawa, Isa Bawa da safiyar yau Alhamis, bayan kashe shi da ƴan bindiga suka yi.

Labarin kisan sarkin ya ɓulla ne a ranar Laraba, bayan da bayanai suka tabbatar da cewa ƴan bindigar sun halaka shi duk da neman kuɗin fansa da suka yi.

Ɗaruruwan mutane ne suka hallara domin gudanar da sallar a garin Sabon Birni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp