Home General Yadda biyan ƴanbindiga kuɗin fansa ke illa ga tsaron Najeriya

Yadda biyan ƴanbindiga kuɗin fansa ke illa ga tsaron Najeriya

Afghan military personnel walk near the airport during fighting between Taliban militants and Afghan security forces in Kunduz on October 1, 2015. Afghan forces pushed into the centre of Kunduz on October 1, triggering pitched gunfights as they sought to flush out Taliban insurgents who held the northern city for three days in a stinging blow to the country's NATO-trained military The stunning fall of the provincial capital, even temporarily, highlighted the stubborn insurgency's potential to expand beyond its rural strongholds in the south of the country Afghan forces, hindered by the slow arrival of reinforcements but backed by NATO special forces and US air support, struggled to regain control of the city after three days of heavy fighting. AFP PHOTO / Wakil Kohsar

Wani rahoto na Kamfanin SB Morgen da ke sa ido kan harkokin tsaro a Yammacin Afirka, ya ce masu garkuwa da mutane a Najeriya sun nemi kusan naira biliyan 10.9 a matsayin kudin fansa daga iyalan wadanda suka sace daga watan Junin 2023 zuwa Yulin 2024.

Rahoton kamfanin wanda takensa shi ne yadda satar mutane ta zama kasuwanci a Najeriya, ya ce daga cikin kudaden da aka nema, ƴanbindigar sun yi nasarar karɓar kimanin naira biliyan daya.

Kusan kullum, ‘yan Najeriya musamman mazauna yankin arewa maso yamma, na cikin fargabar sacewa ko kisa daga ‘yan fashin daji da ke kai hare-hare a kullum.

Rahoton ya ce mutum 7,568 ne aka sace a sassan Najeriya tsakanin Yunin 2023 zuwa Yulin 2024.

Ƴanbindigar da ke satar mutane domin kuɗin fansa sun ƙunshi mayaƙan Boko Haram da ke arewa maso gabashi, da ƴanbindiga da ke cin karensu ba babbaka a arewa maso tsakiya da arewa maso yammaci da kuma ayyukan masu barazanar ɓallewa daga ƙasar a kudu maso kudu.

Rahoton ya ce jihohin Zamfara da Katsina da Kaduna da ke shiyar arewa maso yammaci matsalar ta satar mutane domin kuɗin fansa ta fi yin ƙamari.

Kuma a jihohin guda uku ne aka fi satar kisan mutane, a cewar rahoton na SB Morgen.

Rahoton ya ce a shekarar 2024 kaɗai, an kashe mutum 1,056 ta sanadin ƙoƙarin sace su, yayin da kuma aka saci mutum 1,130.

Rahoton ya ce wani abu da ke ƙara haifar da barazana shi ne yadda ƴanbindigar ke saɓa alƙawali, inda suke kashe mutane duk da an biya su kuɗin fansa.

Ko a makon da ya gabata ƴanbindiga sun kashe Sarkin Gobir na Gatawa Isa Bawa, bayan kwashe makonni a hannunsu suna garkuwa da shi, lamarin da ya girgiza ƴan Najeriya.

Masana tsaro irinsu Malam Kabiru Adamu shugaban kamfanin Beacon Consulting ya ce dole akwai waɗanda ke da alaƙa da ƴanbindigar da suke aiki tare da ke taimaka masu a harkar satar mutane domin karɓar kuɗin fansa.

“duk lokacin da aka ce an samu matsala ta tsaro irin wannan, da wahala ka ga cewa shi ainihin wanda yake yi a ce shi kaɗai ne dole akwai waɗanda ke taimaka masa,” in ji masanin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp