Home DUNIYA Fursunoni 63 sun gurfana gaban kotun Sojin Congo kan laifukan kisa da...

Fursunoni 63 sun gurfana gaban kotun Sojin Congo kan laifukan kisa da fyaɗe

Akalla fursuna 63 sun gurfana a gaban wata kotun Soji da ke tsakiya birnin Kinshasa na Jamhuriya Dimokradiyar Congo a jiya laraba inda za su fuskanci tuhuma kan zarginsu da hanu a kisan mutane 130 da kuma aikata fyade.

Wadanda ake zargin sun bayyana ne a gaban wata kotun sojoji da ke a harabar gidan kason Makala a babban birnin ƙasar Kinshasa.

Lauyoyin fursunonin sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa ana tuhumar mutanen da suke karewa da laifukan lalata gine gine da haddasa gobara da kuma ayyukan ta’addanci baya ga aikata fyade.

A zaman da ta yi na farko a makon jiya an fuskanci rashin fahimtar juna dangane da laifuka da ake zargin mutanen da aikatawa.

A cikin daren 1 wayewar 2 ga watan satumban nan fursunoni da dama sukayi yunkurin tserewa daga gidan kaso ba tare da yin karin haske game da irin yanayin da lamarin ya afku ba.

Alkalumman wucin gadi da gwamnati ta fitar na cewa akalla mutum 129 suka mutu, 24 daga ciki an harbe su ne da bindiga, gabanin washegari mahukuntan kasar su fitar ƙarin adadin mutun biyu da suka mutu sakamakon raunukan da suka ji.

Ƙungiyar Tarayya Turai, da offishoshin jakadancin Faransa da Belguim dukanin su sun bukaci yin haske game da lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp