Fursunoni 63 sun gurfana gaban kotun Sojin Congo kan laifukan kisa da fyaɗe

Akalla fursuna 63 sun gurfana a gaban wata kotun Soji da ke tsakiya birnin Kinshasa na Jamhuriya Dimokradiyar Congo a jiya laraba inda za su fuskanci tuhuma kan zarginsu da hanu a kisan mutane 130 da kuma aikata fyade.

Wadanda ake zargin sun bayyana ne a gaban wata kotun sojoji da ke a harabar gidan kason Makala a babban birnin ƙasar Kinshasa.

Lauyoyin fursunonin sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa ana tuhumar mutanen da suke karewa da laifukan lalata gine gine da haddasa gobara da kuma ayyukan ta’addanci baya ga aikata fyade.

A zaman da ta yi na farko a makon jiya an fuskanci rashin fahimtar juna dangane da laifuka da ake zargin mutanen da aikatawa.

A cikin daren 1 wayewar 2 ga watan satumban nan fursunoni da dama sukayi yunkurin tserewa daga gidan kaso ba tare da yin karin haske game da irin yanayin da lamarin ya afku ba.

Alkalumman wucin gadi da gwamnati ta fitar na cewa akalla mutum 129 suka mutu, 24 daga ciki an harbe su ne da bindiga, gabanin washegari mahukuntan kasar su fitar ƙarin adadin mutun biyu da suka mutu sakamakon raunukan da suka ji.

Ƙungiyar Tarayya Turai, da offishoshin jakadancin Faransa da Belguim dukanin su sun bukaci yin haske game da lamarin.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 13 hours 57 minutes 57 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 15 hours 39 minutes 22 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com