Hare-haren Isra’ila a Beirut sun kashe mutum 22, sun jikkata 117

Ma’aikatar lafiyar Lebanon ta ce wasu jerin gwanon hare-haren da Isra’ila ta kai mata sun yi sanadiyar mutuwar mutum 22, sannan mutum 117 suka jikkata.

An kai hare-haren ne a Bachoura, wanda su ne hare-hare mafiya muni tun farkon fara yaƙin.

Wasu kafofin sadarwa a ƙasar sun ce Wafiq Safa – wanda na hannun damar jagoran Hezbollah Hassan Nasrallah ne, wanda kuma ake tunanin shi ne Isra’ilar take hari – ya tsira daga harin.

Har yanzu da rundunar sojin Isra’ila da Hezbollah babu wanda ya ce komai a game da hare-haren.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com