Home DUNIYA Hare-haren Isra’ila a Beirut sun kashe mutum 22, sun jikkata 117

Hare-haren Isra’ila a Beirut sun kashe mutum 22, sun jikkata 117

Ma’aikatar lafiyar Lebanon ta ce wasu jerin gwanon hare-haren da Isra’ila ta kai mata sun yi sanadiyar mutuwar mutum 22, sannan mutum 117 suka jikkata.

An kai hare-haren ne a Bachoura, wanda su ne hare-hare mafiya muni tun farkon fara yaƙin.

Wasu kafofin sadarwa a ƙasar sun ce Wafiq Safa – wanda na hannun damar jagoran Hezbollah Hassan Nasrallah ne, wanda kuma ake tunanin shi ne Isra’ilar take hari – ya tsira daga harin.

Har yanzu da rundunar sojin Isra’ila da Hezbollah babu wanda ya ce komai a game da hare-haren.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp