Home AFIRKA An rantsar da Kithure a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya

An rantsar da Kithure a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya

Wannan ya biyo bayan hukuncin kotu da ya bada damar rantsar da sabon mataimakin biyo bayan tsige tsohon mataimakin shugaban ƙasar Rigathi Gachagua a watan da ya gabata.

Babbar kotu a Kenya ce ta dakatar da rantsar da Kindiki bayan Gachagua da magoya bayansa sun shigar da ƙarar ƙalubalantar tsigeshi da majalisun dokokin ƙasar biyu suka yi.

To sai dai  a ranar Alhamis kotu ta janye dakatarwar da aka yi na rantsar da Rigathi Gachagua a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya.

Kotun ƙoli a Kenya ce ta bayar da umarnin rantsar da sabon mataimakin shugaban ƙasa, bayan majalisun dokokin ƙasar biyu suka tsige Rigathi Gachagua daga muƙaminsa.

An dai share tsawon watanni ana fama da rikici tsakanin Shugaba William Ruto da mataimakinsa Rigathi Gachagua, to sai dai a ranar 17 ga watan oktoban da ya gabata rikicin ya ɗauki sabon salo inda har ta kai ƙarama da kuma babbar majalisar dokokin dokokin ƙasar suka kaɗa ƙuri’ar kawo ƙarshen mulkinsa.

Wanda ake shirin rantsarwa a wannan juma’a wato ministan cikin gida Kithure Kindiki, mutum ne mai shekaru 52 a duniya, kuma ya yi fice saboda kasancewarsa kasaitaccen malamin jami’a, kafin daga bisani ya tsunduma siyasa daga-gadan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp