Home General Atiku ya magantu kan dokar haraji a Nijeriya

Atiku ya magantu kan dokar haraji a Nijeriya

Jagoran adawar Najeriya, Atiku Abubakar ya yi kira ga majalisar dokokin ƙasar ta yi aiki bisa gaskiya da riƙon amana wajen shirya taron jin ra’ayin jama’a kan sabon ƙudirin harajin ƙasar da ya tsallake karatu na biyu a zauren majalisar.

A makon da ya gabata ne majalisar dattawan ƙasar ta yi wa ƙudirin karatu na biyu, inda kuma yanzu ta miƙa shi ga kwamitin kuɗi na majalisar domin shirya taron jin ra’ayin jama’a kan ƙudurin.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Lahadi, tsohon mataimakin shugaban Najeriya, ya ce kan ‘yan ƙasa ya haɗu wajen yin kira a samar da tsare-tsaren kuɗi bisa adalci da daidaito ga kowane yanki.

”Mun faɗa da babbar murya cewa bai kamata tsare-tsaren kuɗi da gwamnatin ƙasar ke son ingantawa su fifita wasu jihohin ƙalilan ta hanyar ruguza sauran ba”, in ji Atiku Abubakar.

”A matsayina na mai ruwa da tsaki, na yi imanin cewa gaskiya da adalci da riƙon amana da kyakkyawan shugabanci, na da matuƙar muhimmanci wajen tsara manufofi”.

Majalisar dattawan ƙasar ta ce ta amince da ƙudirin ne a karatu na biyu domin bayar da dama a shirya sauraron ra’ayin jama’a a kansa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp