Home General Jihohi biyu ne kaɗai za su amfana da sabuwar dokar harajin Najeriya...

Jihohi biyu ne kaɗai za su amfana da sabuwar dokar harajin Najeriya – Zulum

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya bayyana dalilin da ya sa gwamnonin Arewa suka shawarci shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya ɗan dakata kafin ya tura daftarin dokar sake fasalin harajin ƙasar zuwa majalisar dokoki.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da gidan Talabijin na Channels ranar Lahadin da ta gabata, ya ce ƙungiyar gwamnonin Arewa na buƙatar lokaci ne domin tuntuɓa da kuma nazarin ɓangarorin dokar harajin.

“A kan wannan dokar, akwai abubuwa da dama da ba a fahimta ba. Mun duba tanadin da aka yi wa harajin VAT a cikin dokar. Bisa kididdigar da muka yi, Jihohin Legas da Ribas ne kaɗai za su ci gajiyar waɗannan sauye-sauyen. Mun yi namu binciken kuma mun gano cewa za mu yi asara,” inji Zulum.

“Me yasa muke hanzari? Mun shawarci Gwamnatin Tarayya da ta dakata, ta yi kakkaɓe wasu abubuwan da za su iya cutar da yankin Arewacin Najeriya.”

Zulum ya yi bayanin cewa idan har dokar ta sami amincewar Majalisar Dokoki ta kasa, za a cutar da jihohi da dama domin jihar Legas ce kaɗai za ta ci gajiyar wannan manufa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp