Home General An samu ƙaruwar gobara a Kano saboda shigowar sanyi

An samu ƙaruwar gobara a Kano saboda shigowar sanyi

Hukumar kashe gobara a Kano ta ce an samu ƙarin tashin gobara a faɗin jihar sakamakon shigowar yanayin hunturu a wasu yankunan a jihar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Kakakin hukumar Saminu Yusuf Abdullahi ya fitar aka raba manema labarai a a jihar da ke arewa maso yammacin Nijeriya in da ya ce kafin zuwan yanayin hunturun an samu raguwar tashin gobara a jihar – wadda ita ce cibiyar kasuwancin arewacin ƙasar.

Saminu Yusuf Abdullahi ya ce a watan Nuwamban da ya gabata kaɗai an samu tashin gobara a jihar har sau 43, sakamakon yadda mutane ke ƙara ta’ammali da wuta a lokacin na hunturu.

”Adadin ya ninka, domin a watan Oktaba an samu matsalar tashin gobara a Kano sau 24, amma sakamakon shigowar hunturu a watan Nuwamban adadin ya kai 43”, in ji shi

Ya kuma ce daga shigowar watan Disamba, zuwa yanzu hukumarsu ta samu labarin tashin gobara har sau bakwai, zuwa yanzu.

Haka kuma hukumar kashe gobarar jihar ta ce mutum uku sun mutu, yayin da aka yi asarar dukiya da ta kai naira miliyan 130, a cikin watan da ya gabatan sakamakon tashin gobarar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp