Home General Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia

Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia

Mai lamba ta 6 a duniya Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia za ta buga da Denmark sakamakon rauni a kafarsa

Rauni ya tilasta Djokovic, mai shekaru 37, ficewa a wasan kusa da na karshe na gasar Australian Open da Alexander Zverev na Jamus a makon jiya saboda raunin da ya samu, inda magoya bayansa a Melbourne suka yi masa ihu.

Zakaran na Grand Slam na sau 24 ya saka hoton gwajin MRI da aka yi masa a kafarsa ta hagu a shafukan sada zumunta inda ya rubuta cewa ya saka wannan ne domin masana raunin ƴan wasa su gani domin tabbatar da yanayin da ya sa shi ya fice daga gasar.

Serbia, wacce za ta yi rashin Djokovic, za ta kara da Denmark a wasan share fage na zagayen farko, wanda za a fara ranar Juma’a 31 ga watan Janairu.

Kyaftin din Serbia Viktor Troicki ya ce sun samu rauni na rashin Novak, amma har yanzu suna da ƙwarin gwiwar samun nasara.

Denmark suna da babban dan wasa, wato Holger Rune, amma ‘yan wasansu ma suna da kyau kuma ya yi imani da tawagarsu.

Tawagar Serbia yanzu ta ƙunshi Miomir Kecmanovic, Hamad Mededovic, da Laslo Dere, da kuma ƙwararrun ƴan double ‘yan’uwan Sabanov, Matej da Ivan.

Haka kuma Serbia za ta kasance ba tare da Dusan Lajovic ba saboda rauni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp