Bincike: Shin da gaske ne Tsohon shugaban Nijeriya Buhari, ya dogara da kudin hayar gidajensa da yake karba bayan ya kammala wa’adin mulkinsa na shugabancin kasa?

Ikirari: An ruwaito cewa Shugaban Nijeriya Muhammadu ya ce ya laru (dogara) da kudin da yake karba na hayar gida daya daga cikin gidajensa biyu da ya mallaka a jihar Kaduna domin gudanar da rayuwarsa ta yau da kullum byan ya kamala wa’adin mulkinsa na biyu matsayin shugaban kasar Nijeriya.

Wannan labarin ya bayar mutane da dama cikin rudani, idan ya fadi hakan abin ne da zai iya kasancewa musamman a wajen da ake kallonsa cikin mutane masu gaskiya da amana da basa iya boye gaskiya da sai sun furta.

‎masu karatu da dama sun musanta labarin, inda suke cewa: “ta ya hakan zai kasance gaskiya? A matsayinsa na tsohon Janar din soja da yayi ritaya, yana karbar kudi sama da miliyan 1 dukkan wata matsayin Fansho, ga kuma tanadin da aka yiwa tsuffin shuwagabannin kasa da shugabannin mulkin soji. Kai akwai lauje cikin nadi a wannan zance.”

‎Muhammada Buhari ya mulki Nijeriya a matsayin shugaban mulkin soji a shekarar 1983 zuwa 1985, lokacin da ya hambarar da gwamnatin shugaban kasa Shehu Shagari a wani juyin mulki a shekarar 1983. A lokacin da yake matsayin shugaban kasa Buhari ya gabatar da tsare-tsare masu tarin yawa domin yakar cin hanci da rashawa, yaki da rashin da’a wato (War Againts Indiscipline) a shekarar 1984, shirin da yayi shuhura wajen inganta tarbiyya da da’a cikin Al’ummar Nijeriya.

‎haka kuma shugaban Muhammadu Buhari ya sake mulkar Nijeriya a shekarar 2015 zuwa 2023, karkashin inuwar jam’iyyar APC. Shugabancin sa ya bayyana yunkuri mai yawa wajen yakar cin hanci da rashawa, habaka tattalin arziki, tare da inganta sha’anin tsaro a fadin kasar.

Bincike Sahihancin Labari: Domin tabbatar gaskiyar ikirarin, tawagar PRNigeria dake binciken sahihanci labarai, ta sanya wannan ikirarin da aka wallafa a wata jarida a ranar  27 ga watan janairu,2025 a na’ura.

Tawagar ta gano, tsohon shugaban kasar yayi irin wannan ikirari a taron Caucus da jam’iyyar APC ta shirya da ya gudana a dakin taro na Presidential Banquet Dake fada gwamnatin jihar Katsina.

‎“Nijeriya kasa cewa mai wahalar shugabanta, amma da dama cikin al’ummar kasa basu fahimci haka ba. Baza ka fahimci wahakar shugabancin kasar ba, har sai ka tsinci kanka matsayin shugaban kasa a kasar.

“Na fi kyawun gani da ingantacciyar lafiya yanzu, akan lokacin ina shugaban kasa. Dukkan wanda ya gani a yanzu zai tabbatar da cewa nafi kyan gani a kan baya.

“bayan kamala wa’adin shekaru 8 a matsayin shugaban kasa a mulkin farar hula, na mallaki gidaje guda uku kawai; daya a Daura, biyu a jihar Kaduna. Na bayar da hayar guda daya daga cikin su, inda nake samun kudin da zan ci abinci”. A cewar sa.

Wani bincike ya tabbatar da a shekarar 2016, Buhari ya yi bayanin irin wannan inda ya ce baya samun fanshonsa bayan ya yi ritaya a matsayin babban soja, kamar yadda abokan aikinsa da suka kamala aiki tare suke samu.

Amma kuma, Gwamnatin tarayya ta ware wasu makudan kudade da suka kai naira biliya. 7.8 cikin kasafin kasar, wanda ta ce domin ta biya tsoffin shuwagabannin kasar da mataimakansu da sauransu a shekarar 2021. Kamar yadda kasafin kudin shekarar 2021 da aka amince da shi ya bayyana, a kalla naira biliyan 7.8 aka ware domin biyan alawus-alawus da sauran hakkoki ga tsofaffin shugababannin kasar.

‎kudin da aka ware a shekarar 2021 shine na biyu mafi kankanta a cikin kudaden da aka ware da shugabannin mulkin soji da shugabannin kasa tun shekarar 2017, yayin da aka ware naira biliyan 5.9 matsayin garatuti. Sai kuma a shekarar 2021 da aka ware naira biliya 7.8 ga tsofaffin shuwagabannin kasa da tsofaffin shuwagabannin mulkin soji da mataimakansu suka karbi hakkokinsu da yasa kai naira biliyan 2.3

‎Haka kuma hukumar wayar da kai da lura da raba arziki kasa ta (RMFAC) ta amince dukkan tsohon shugaban kasa zai sami naira miliyan 10.54, wanda ya zama kashi 300 cikin 100 na alabashinsa na shekara, shi kuma mataimakain shugaban kasa zai sami miliyan 9.09.

Bugu da kari, dokar ta bayyana cewa, dukkan tsohon shugaban kasa zai sami alawus din gida naira dubu 350, ya yin da tsohon mataimakin shugaban kasa da tsoffin shuwagabannin sojin kasa zasu sami naira dubu 250,000. Akwai dama sake dubawa domin yin kari idan aka yi kari kan albashin shugaban kasa.

‎a ‘yan tsakaninnan gwamnatin bisa jagorancin Tinubu ta ware naira 13,805,814,220, domin biyan kudin gidajen zama ga tsofaffin shuwagabanni, Mataimakansu, shugwabannin mulkin soji, shuwagabannin tsaron soji, da kuma shugabannin ma’aikata, Manyan sakatarori da kuma shugabannin hukumomin da ma’aikatun gwamnatin tarayya da sukayi ritaya a shekarar 2024.

Wadanda zasu rabauta da kudin sun hadar da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, Goodluck Jonathan da Muhammadu Buhari, sai kuma tsofaffin Mataimakan shugaban kasa da suka hadar da Atiku Abubakar, Namadi Sambo da farfesa Yemi Osibanjo

Ana kuma tsammanin tsofaffin shuwagabannin mulkin soji da suka hadar da Janar Yakubu Gowon, Janar Abdusalami Abubakar, da Janar Ibrahim Badamasi Babangida da kuma shugaban rundunar sojin kasar Commodore Ebitu Ukiwe mai ritaya.

Ko da yake, tun da shugaba Buhari ya yi wannan ikirarin na cewa yana da gidaje 3 kadai daya a Daura, biyu kuma a jihar Kaduna, wanda kuma a cikin su ne ya bayar da daya haya, domin ya samu kudin da zai ci abinci da iyalensa, a shekarar 2015, yayi da yake bayar da hakikanin yawan dukiyar da ya mallaka kafin ya zama shugaban kasa, ya bayyana cewa ya mallaki gidaje guda biyar da kuma gidan kasa guda biyu, sannan yana da gona da ke da tarin bishiyo da garken shanu 270, tumaki 25, Dawakai 5, da kuma tarin tsuntsaye. Haka kuma yana da hannun jari a gidajen gona guda 3, sannan yana da filaye da ba’a gina ba guda 2, sai kuma mutoci guda biyu da ya siya a cikin kudin da yake adanawa, haka kuma ba’a bayyana dukiyar sa a shekarar 2023 ba har ya sauka daga shugabancin kasar.

A Takaice: PRNigeria ta gano cewa tsohon shugaba Muhammadu Buhari yana samun kudi dukkan wata daga rundunar sojojin Nijeriya a matsayinsa na tsohon Janar mai ritaya, matsayin tsohon shugaban kasa na mulkin soji. Haka kuma a ikirarinsa da ke cewa yana da gidaje guda uku rak a jihar kaduna wanda a cikinsu ya bayar da guda daya haya, kuma da shi ya dogara bayan ya kamala wa’adin sa na biyu a matsayin shugaban kasar Nijeriya. Kadarorin Buhari da kowa ya sani dai sun hadar da gidaje guda biyar da kuma gidan kasa guda biyu, sannan yana da gona da ke da tarin bishiyo da garken shanu 270, tumaki 25, Dawakai 5, da kuma tarin tsuntsaye. Haka kuma yana da hannun jari a gidajen gona guda 3, sannan yana da filaye da ba’a gina ba guda 2, sai kuma mutoci guda biyu da ya siya a cikin kudin da yake adanawa.

PRNigeria ta tabbatar da cewa ikirarin tsohon shugaban kasa Muhammadu na cewa ya dogara da kudin haya da yake samu daga gidansa da ya bayar a jihar kaduna ba gaskiya bane

PRNigeria

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 2 hours 24 minutes 11 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 4 hours 5 minutes 36 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com