Jami’ar Al-istiqama da ke garin Sumaila ta nada sabon Sarkin Dutse Alhaji Muhammad Hamim Sunusi a matsayin sabon chancilor.
Naɗin nasa wanda ya gudana a masarautar Dutse a yau Alhamis 6 ga watan Fabrairu 2024, na zuwa ne biyo bayan karewar wa’adin Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero.
Read Also:
Da yake miƙa takardar naɗin mamallakin Jami’ar Sanatan Kano ta Kudu Sulaiman Abdulraman Kawu Sumaila, ya bayyana daɗaɗɗiyar alaƙarsu da masarautar Dutse, wanda hakan ya sanya hukumar gudanarwa jami’ar taga dacewar baiwa Mai martaba Sarkin Dutse dama domin zama Chancellor na Jami’ar, duba da yadda masautar ke baiwa addinin musulunci muhimmanci matuƙa dai dai da yadda aka ɗora manufar gudanar da Jami’ar.
Da yake jawabi mai martaba sarkin Dutse Alhaji Muhammad Hamim Nuhu Sunusi, ya nuna jin daɗinsa bisa karrama masarautar tare da godewa wanda ya assasa jami’ar da sauran hukumomin gudanarwarta.
Ya kuma ƙara da cewa tun abaya sun san za’azo wannan gaɓa duba da irin alaƙa ta mutunci da girmanawa dake tsakanin masarautar da yankin Sumaila.
Sarkin ya kuma yi alƙawarin bada gudunmawar masauatar ɗari bisa ɗari domin ci gaban wannan jami’a dama al’umma baki ɗaya.
Zuwa yanzu dai jami’ar ta samu sahalewar gudanarwa na din-din-din daga hukumar dake kula da jami’o’i ta ƙasa NUC bayan tsallake zangon gwaji da jami’ar tayi na tsawon shekaru.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 2 hours 16 minutes 29 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 3 hours 57 minutes 54 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com