Home General Sarki Dutsen ya Zama Uban Jami’ar Al-Istiqama

Sarki Dutsen ya Zama Uban Jami’ar Al-Istiqama

Jami’ar Al-istiqama da ke garin Sumaila ta nada sabon Sarkin Dutse Alhaji Muhammad Hamim Sunusi a matsayin sabon chancilor.

Naɗin nasa wanda ya gudana a masarautar Dutse a yau Alhamis 6 ga watan Fabrairu 2024, na zuwa ne biyo bayan karewar wa’adin Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero.

Da yake miƙa takardar naɗin mamallakin Jami’ar Sanatan Kano ta Kudu Sulaiman Abdulraman Kawu Sumaila, ya bayyana daɗaɗɗiyar alaƙarsu da masarautar Dutse, wanda hakan ya sanya hukumar gudanarwa jami’ar taga dacewar baiwa Mai martaba Sarkin Dutse dama domin zama Chancellor na Jami’ar, duba da yadda masautar ke baiwa addinin musulunci muhimmanci matuƙa dai dai da yadda aka ɗora manufar gudanar da Jami’ar.

Da yake jawabi mai martaba sarkin Dutse Alhaji Muhammad Hamim Nuhu Sunusi, ya nuna jin daɗinsa bisa karrama masarautar tare da godewa wanda ya assasa jami’ar da sauran hukumomin gudanarwarta.

Ya kuma ƙara da cewa tun abaya sun san za’azo wannan gaɓa duba da irin alaƙa ta mutunci da girmanawa dake tsakanin masarautar da yankin Sumaila.

Sarkin ya kuma yi alƙawarin bada gudunmawar masauatar ɗari bisa ɗari domin ci gaban wannan jami’a dama al’umma baki ɗaya.

Zuwa yanzu dai jami’ar ta samu sahalewar gudanarwa na din-din-din daga hukumar dake kula da jami’o’i ta ƙasa NUC bayan tsallake zangon gwaji da jami’ar tayi na tsawon shekaru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp