Gwamnan Kano ya nada sabon sakataren Gwamnatin jihar

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nada Umar Farouk Ibrahim a matsayin sabon sakataren gwamnatin jihar Kano (SSG).

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar Kuma aka raba manema labarai a jihar

Nadin Ibrahim zai fara aiki daga ranar Litinin 10 ga Fabrairu, 2025.

Sanarwar ta ce, an zabi Ibrahim ne bisa gogewar da yake da ita, wanda ake sa ran zai yi amfani da ita wajen inganta harkokin gwamnatin jihar Kano.

Umar Farouk Ibrahim da ta kwashe sama da shekaru talatin yana aikin gwamnati , don haka ake fatan zai kawo cigaba sosai a sha’anin tafiyar da harkokin aikin gwamnati.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 6 hours 41 minutes 2 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 8 hours 22 minutes 27 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com