Home General Tinubu ya yaba wa El-Rufai saboda ‘gina dimokraɗiyya’ a Najeriya

Tinubu ya yaba wa El-Rufai saboda ‘gina dimokraɗiyya’ a Najeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yaba wa tsohon gamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai kan gudunmowar da ya bayar a fannin dimoƙraɗiyyar ƙasar.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, domin taya El-Rufai munar cika shekara 65 a duniya, Tinubu ya bayyana tsohon gwamnan na Kaduna da jagora, manazarci kuma ɗan siyasa.

”Irin gudunmowar da ya bayar wajen hidimta wa ƙasa da zama abin koyi ga ƴan baya, babban abin yabawa ne”, a cewar sanarwar.

Shugaba Tinubu ya kuma yaba wa rawar da El-Rufai ya taka wajen kafuwar jam’iyyar APC, da kuma irin gudunmowar da ya bayar wajen nasarorin jam’iyyar a zaɓukan ƙasar uku da suka gabata, 2015 da 2019 da kuam 2023.

A shekarar 2015 ne aka zaɓi Mallam Nasir El-Rufai a matsayin gwamnan jihar Kaduna, inda ya yi wa’adin mulki biyu.

Bayan rantsar da Shugaba Tinubu a 2023 ya sanya sunan El-Rufai cikin jerin mutanen da yake son bai wa muƙaman ministoci, sai dai tsohon gwamnan bai tallake tantancewar majalisar dattawan ƙasar ba, lamarin da ya sa bai samu muƙamin ba.

Daga nan ne kuma dangantaka ta fara tsami tsakaninsa da Tinubu, inda a baya-bayan ya riƙa fitowa fili yana sukar manufofin gwamnatin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp