Home General Tinubu ya yaba wa El-Rufai saboda ‘gina dimokraɗiyya’ a Najeriya

Tinubu ya yaba wa El-Rufai saboda ‘gina dimokraɗiyya’ a Najeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yaba wa tsohon gamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai kan gudunmowar da ya bayar a fannin dimoƙraɗiyyar ƙasar.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, domin taya El-Rufai munar cika shekara 65 a duniya, Tinubu ya bayyana tsohon gwamnan na Kaduna da jagora, manazarci kuma ɗan siyasa.

”Irin gudunmowar da ya bayar wajen hidimta wa ƙasa da zama abin koyi ga ƴan baya, babban abin yabawa ne”, a cewar sanarwar.

Shugaba Tinubu ya kuma yaba wa rawar da El-Rufai ya taka wajen kafuwar jam’iyyar APC, da kuma irin gudunmowar da ya bayar wajen nasarorin jam’iyyar a zaɓukan ƙasar uku da suka gabata, 2015 da 2019 da kuam 2023.

A shekarar 2015 ne aka zaɓi Mallam Nasir El-Rufai a matsayin gwamnan jihar Kaduna, inda ya yi wa’adin mulki biyu.

Bayan rantsar da Shugaba Tinubu a 2023 ya sanya sunan El-Rufai cikin jerin mutanen da yake son bai wa muƙaman ministoci, sai dai tsohon gwamnan bai tallake tantancewar majalisar dattawan ƙasar ba, lamarin da ya sa bai samu muƙamin ba.

Daga nan ne kuma dangantaka ta fara tsami tsakaninsa da Tinubu, inda a baya-bayan ya riƙa fitowa fili yana sukar manufofin gwamnatin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp