Ikirari: wani faifen bidiyo da ake yadawa a kafar sada zumunta ta zamani na ikirarin cewa mayakan kungiyar boko haram na sake tattara kawunansu don sake haduwa a yankin arewa maso gabashin Nijeriya.
Faifen bidiyon da aka hada shi da rubutun dake cewa “wannan shine abinda zulum ke Magana a kai. Tattara mayakan boko haram guri guda domin hade kawunansu a yankin arewa maso gabas.” Ikirarin ya kuma tabbatar da cewa dama gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya yi gargadin faruwar hakan.
A makonnin da suka gabata, Zulum ya bayyana damuwarsa bisa yunkurin dawowar kungiyar boko haram sakamakon wasu hare-hare da kungiyar ta gudanar, tare da zargin cewa kungiyar na iko da wasu yankuna a yankin na Arewa Maso gabas. Haka kuma ya bukaci Karin dakarun sojoji a yankin domin yakar matsalolin rashin tsaro dake addabar Al’umma.
Jihar Borno ta kwashe shekaru 15 ta na fama da matsalar boko haram, lamarin da ya raba mutane sama da miliyan biyu da muhallansu tare da hallaka sama da dubu dakkan musulmai da Kirista. Ko a shekarar 2015 mayakan na boko haram sun sami iko da wasu yankuna masu yawa kafin dakarun sojoji su yi kokarin fatattakar su.
Tantancewa: PRNigeria ta gudanar da binciken sahihancin labara ta hanyar yin amfani da manhajar binciken hotuna ta (reverse image search) kan faifen bidiyon dake nuna dakaru wasu fuskokinsu a rufe wasu kuma na bisa Babura da motar Hilux mallakin sojoji a sahara.
Sai dai PRNigeria ta gano harshen da ake amfani da shi a bidoyon ba Hausa bane ko Larabci, kuma ba Harshen kanuri bane, harshen da manyan shuwagabannin kungiyar Boko haram irin su Muhammad Yusuf da Abubakar Shekau suka yi amfani da shi wajen yada Farfaganda a bidiyoyinsu. Wannan ya sanya shakku wajen tabbatar da sahihancin bidiyon.
Read Also:
Haka kuma wani bincike ya bayyana cewa yanayin muhallin da tsarin bushewarsa ya saba da yadda tsarin dajin Sambisa yake, wanda ya kasnce mai Laima da sanyi, wanda kuma shine sansanin mayakan boko haram.
Dajin Sambisa ya na jihar Borno, daji ne da kogunan Ngadda da Yedseram suka ratsa ta cikinsa wanda yake da fadin kilomita 518 Km2. Ya taba zama guda cikin wuraren bude idanu, sai dai kuma da ga baya ya zama wata maboyar masu tada kayar baya, amma dai bshi da yanayi na sahara kamar yadda aka gani a wancan bidiyon.
Manhajar binciken hoton ta PRNigeria ta bayyana cewa bidiyon na Mayakan Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM) kungiyar tada kayar baya dake yankin Sahel wadanda ke gudanar da ayyukan ta’addanci a kasar Burkina Faso. Kamar yadda zagazola Makama ya tabbatar a wata wallafa da yayi a a shafinsa na X wanda aka fi sani da twitter.
Bidiyon bashi da alaka da jihar Borno ko kuma boko haram, haka kuma alakanta shi da kalaman Zulum ka iya zama an sauya ma’anar labarin wanda hakan na da hadarin gaske.
JNIM wata hadaddiyar kungiya ce ta masu bin manhaji salafiyya da aka kafa ta a shekarar 2017 sakamakon hadewa da kungiyoyi masu tsattatsauran ra’ayi da suka hadar da Ansar al-Din, al-Murabitun, Macina Liberation Front (MLF), da kuma Sahara Emirate subgroup of al-Qa‘ida in the Islamic Maghreb (AQIM) suka yi bisa jagorancin Iyad ag Ghali, JNIM na da alaka da kungiyoyin al-Qa‘ida da Taliban wadanda suke gudanar da ayyukansu a kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Jamhuriyyar Niger, wadanda suka yada tsatstsauran ra’ayi.
A takaice: Bidiyon da aka yada dake cewa mayakan Boko haram na sake hade kawunan su a Nijeriya, wanda kuma mayakn na Kungiyar JNIM da ke Burkina Faso ne, wanda kuma basu da alaka da kalaman Gwamna Zulum kan matsalar rashin tsaro.
Hukunci: PRNigeria ta tabbatar da cewa ikirarin da aka yi cewa mayakan kungiyar Boko haram na sake haduwa a yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya, kamar yadda aka nuna a bidiyon, ba gaskiya bane (Karya Ne).
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1461 days 21 hours 24 minutes 31 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1443 days 23 hours 5 minutes 56 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com