Home General ‘Yanbindiga sun sace mutum 117 da hallaka wasu tara a Jihar Kebbi

‘Yanbindiga sun sace mutum 117 da hallaka wasu tara a Jihar Kebbi

Rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa wasu ‘yanbindiga sun hallaka akalla mutane tara sannan kuma suka yi awon-gaba da wasu magidanta 117, a garin Danmuntari da ke yankin Danko-Wasagu a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin kasar.

Wasu mazauna garin da suka tsira daga harin sun tabbatar wa da BBC, cewa lamarin ya faru ne a yammacin ranar Talata, 27 ga watan Mayun, 2025, lokacin da ‘yanbindigan su ka yi wa garin kofar-rago.

Daga cikin wadanda barayin dajin suka kashe har da wata mata mai jego da jaririnta, inda suka harbe su tare da sauran jama’ar da suka hallaka ta hanyar harbin kan-mai-uwa-da-wabi a lokacin da suka shiga garin, kamar yadda shedun suka yi bayani.

”Da la’asar barayin suka kewaye garin suka dinga harbe-harbe wanda hakan ya sa dole mutanen garin suka watse suka cimma na kashewa, suka kashe mutum tara,”in ji daya daga cikin mutanen garin.

Ya kara da cewa, ”Abin ban tausayi akwai mace daya da ba ta wuce sati biyu da haihuwa ba suka kashe ta da ita da jaririnta.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp