Home General NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta NDLEA a Najeriya, ta bankaɗo muggan ƙwayoyi da aka ɓoye a wasu manyan ɗakunan ajiyar kayayyaki da kuɗinsu suka tasama sama da naira biliyan shida da miliyan 700 a jihar Lagos.

Wata sanarwa da daraktan sashen yaɗa labarai na hukumar, Femi Babafemi ya fitar tace, yayin samamen da jami’an NDLEA ɗin suka gudanar, sun kuma cafke wani babban dillalin ƙwaya mai suna Onyekachi Pius tare da wasu mutum biyar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, an samu mutanen da aka cafke ɗauke da waɗannan ƙwayoyi a tattare da su, bayan samamen da aka kai maɓoyarsu da ke wani rukunin gidajee da ke Lagos.

Daga cikin kayayyakin da aka gano a hannun su, akwai maganin Tramadol da kuma kodin, wanda ake zargin sun adana ne saboda bikin Kirismeti da ke ƙaratowa.

A cewar NDLEA, manyan motoci aka yi amfani da su wajen fitar da tarin waɗannan muggan ƙwayoyin daga rukunin gidaje na Festac da ke yankin Apple Junction.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp