Home General ‘Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026’

‘Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026’

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa sama da ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a wannan shekara, saboda rage tallafin da ake bayar wa a duniya.

MDD ta ce kusan yara miliyan uku na barazanar rasa abinci mai gina jiki, inda tuni ake cikin mawuyacin hali a jihohin Borno, Yobe da kuma Adamawa waɗanda rikici ya ɗaiɗaita.

Kodinetan hukumar ba da agaji na MDD a Najeriya, ya ce yanzu ba za a iya dogaro da agajin da aka saba bayar wa ba.

Hukumar ta ce yanzu za ta mayar da hankali ne kawai kan ayyukan ceton rai, inda za ta samar da kusan dala 500,000 don taimakawa mutane miliyan biyu da rabi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp