Rahotanni daga Nijeriya na bayyana cewa Mutane 214 ne suka mutu tsakanin watan Janairu da Maris din shekarar 2023, a hare-haren ‘yan bindiga da rikicin ƙabilanci da hare-haren ɗaukar fansa a jihar Kaduna a Najeriya.

A cikin wannan adadi 14 mata ne a yayin da huɗu yara ne ‘yan ƙasa da shekaru 18.

A gundumar Kaduna ta Tsakiya, an samu rahoton mutuwar mutane 115 (kashi 54 bisa dari na yawan adadin).

Ɗari da takwas na waɗannan adadi sun faru ne a yankunan ƙananan hukumomin Birnin Gwari, da Giwa, da Igabi, Chikun da kuma Kajuru.

Ƙananan hukumomi Giwa da Birnin Gwari duka sun samu yawan adadin mutane 32 da suka mutu, karamar hukumar Chikun 25, Igabi 13, sai Kajuru shida a watannin ukun farkon shekarar 2023.

A yankin kudancin Kaduna an samu mutuwar mutane 61 a daidai irin wannan lokaci.

Yanayin kai hare-hare da na daukar fansa, da munanan tashe-tashen hankula na addini da na kabilanci – tsakanin hare-haren ‘yan bindiga – sun faru a karamar hukumar Zangon Kataf, inda mutane 19 suka rasa rayukansu.

Mutane 12 ne kuma aka kashe a ƙaramar hukumar Sanga a cikin watanni ukun farko na shekarar 2023.

Yankin arewacin jihar ya shaida mutuwar mutane 38 a watanni ukun farko, inda aka samu mutuwar mutane 22 a karamar hukumar Zaria.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp