Home DUNIYA Fiye da mutum 40 sun mutu bayan fashewar madatsar ruwa a Kenya

Fiye da mutum 40 sun mutu bayan fashewar madatsar ruwa a Kenya

Mutane da dama sun rasa rayukansu bayan fashewar wata madatsar ruwa a yankin Mai Mahiu da ke Kenya, kamar yadda ƙungiyar agaji ta Kenya Red Cross ta shaida wa BBC.

Gwamna a yankin, Susan Kihika ma ta tabbatar da mutuwar mutanen ga kamfanin dillancin labarai na AFP.

Ruwa ya ɓalle inda ya tafi da gidaje da motoci da dama a ƙauyen Kamuchiri sakamakon mamakon ruwan sama da ake yi a yankuna da dama na ƙasar.

Tawagar agaji na lalube cikin taɓo domin zaƙulo masu sauran numfashi, in ji kafafen yaɗa labaran ƙasar inda kuma suka yi gargaɗin adadin mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa.

Lamarin ya datse babban titin da ya tashi daga Nairobi zuwa Mai Mahu bayan da manya-manyan duwatsu da taɓo suka rufe hanyar.

Tun farko, ƙungiyar agaji ta Kenya Red Cross ta ce ta kai mutane da dama zuwa asibiti a Mai Mahiu saboda ambaliya.

Adadin mutanen da suka mutu a yanzu sakamakon mamakon ruwan sama da ambaliya a ƙasar tun watan da ya gabata sun zarce 100.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp