Home General Adadin mutanen da ambaliya ta kashe a Maiduguri ya kai 30- NEMA

Adadin mutanen da ambaliya ta kashe a Maiduguri ya kai 30- NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa a Najeriya NEMA ta fara tattara alƙaluman mutanen da suka rasa rayukansu  bayana aukuwar  ibtila’in ambaliyar ruwan a birnin Maiduguri na jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya a cikin daren Talatar da ta gabata.

Mahukuntan jihar sun ce zuwa yanzu an tattara gawarwakin mutane 30 yayin da NEMA ke ci gaba da aikin laluben waɗanda suka maƙale a saman rufin gidaje da wurare masu haɗari.

Hukumar NEMA ta ce ambaliyar ta shafi mutane miliyan 1 da rabi waɗanda ke halin tsananin buƙatar agaji, musamman ganin yadda suka bar muhallansu a yanayi na ɗimuwa sakamakon mummunar ambaliyar wadda ta faro da tsakaddaren Talata.

Kakakin hukumar ta NEMA Ezekiel Manzo ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa kawo yanzu mutane 30 suka tabbatar da mutuwarsu ko da ya ke alƙaluman ka iya ƙaruwa sakamakon yadda har yanzu aka gaza gano mutane da dama da suka bace a ruwan.

Tun farko ɓallewar madatsar ruwa ta Alau ita ta haddasa tumbatsar ruwa a tituna da magudanan Maiduguri wanda zuwa yanzu ya lalata tarin kadarorin da ba a kai ga ƙiyasin ƙudinsu ba, baya ga ginaku da gidajen jama’a da kuma wuraren kasuwanci.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp