Home SIYASA Kotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu...

Kotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4

inec

Kotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4

Wata babbar Kotun Tarayyar Najeriya ta umurci hukumar zaɓen ƙasar INEC ta soke rajistar jam’iyyar adawa ta ADC da wasu jam’iyyu huɗu.

Kotun da ke Abuja ta ce jam’iyyun sun gaza cika sharuɗan da kundin tsarin mulkin kafa jam’iyyun siyasa.

Mai Shari’a Peter Lifu ne ya yanke hukuncin, inda ya ce jam’iyyun ba su samu kashi 25 cikin 100 na ƙuri’un da doka ta tanada a zaɓukan da suka gabata ba.

Jam’iyyun da hukuncin ya shafa su ne ADC, Accord, AA, APP da ZLP. Ya bayyana cewa jam’iyyun taka sashe na 225 na kundin tsarin mulkin Najeriya.

Kotun ta kuma umarci INEC da kada ta bari jam’iyyun su shiga zaɓuka masu zuwa, ciki har da babban Zaɓen 2027, matuƙar ba su cika sharuɗan da doka ta tanada ba.

Wata ƙungiyar tsofaffin ƴan majalisa ta shigar, inda ta yi zargin cewa jam’iyyun sun kasa cika ƙa’idojin da suka shafi samun goyon baya da kuma sakamakon zaɓe.

Sai dai jam’iyyar ADC ta fitar da sanarwar cewa za ta shiga zaɓen 2027 kuma tana kira ga mabiyanta da su yi watsi da hukuncin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 
X whatsapp