Home SIYASA Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu 

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu 

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu 

 

Atiku ya ce kada ’yan ADC kada su karaya, “gwagwarmayar ceto Najeriya ba ta za ta ta’allaƙa kan hukuncin kotu guda ɗaya ba.

A jiya Litinin ce Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta tabbatar da hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ya haramta wa INEC amincewa ko halartar tarukan zaɓen shugabannin jihohin da kwamitin riƙon ƙwaryar ya shirya, tare da tabbatar da ci gaba da wa’adin shugabannin jihohin da aka zaɓa tun da farko.

Sai dai da take mayar da martani, ADC ta ce ta fara shirin ɗaukaka ƙarar, tana mai cewa ba ta yarda da hukuncin ba kuma tana ganin bai dace da doka ba.

Shi ma Atiku Abubakar, ta bakin mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Phrank Shuaibu, ya ce ya umarci lauyoyinsa su garzaya Kotun Ƙoli domin neman hukunci na ƙarshe kan lamarin.

Atiku ya ce saɓanin yadda wasu ke yaɗawa, hukuncin kotun bai soke zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ADC ta gudanar domin tsayar da ’yan takararta a Zaɓen 2027 ba.

Ya ce “abin da wasu ke yaɗawa cewa hukuncin ya kawo ƙarshen takarar shugaban ƙasa ta ADC wani yunƙuri ne na yaɗa bayanan da ba su dace ba domin raunana ƴan adawa da kuma ruɗar da ’yan Najeriya.”

Atiku ya bayyana cewa hukuncin kotun ya shafi zaɓen shugabannin jam’iyyar a matakin ƙananan hukumomi ne da kuma wa’adin shugabannin kwamitocin riƙo na jihohi, ba zaɓen fidda gwani na tsayar da ’yan takara ba.

Ya kuma buƙaci magoya bayan ADC kada su karaya, inda ya ce “gwagwarmayar ceto Najeriya ba ta za ta ta’allaƙa kan hukuncin kotu guda ɗaya ba.”

 

 

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dr Lawan Sani: Yadda Masanin Tsaron Intanet Ya Zama Sarkin Gumel: Daga Shuaib S. AgakaAllah ne Kawai Zai Iya Hana Tinubu Cin Nasara a 2027 — Datti"Dangantakar Farar Hula da Sojoji Itace Mabuɗi ga Tsaron Ƙasa da Shugabanci Nagari" — Tsohon CDS IraborRundunar Sojin Najeriya ta Binciki Zargin Cin Zarafin Jima'i da Aka yi wa Kyaftin a JosBabban Jami’in EFCC na Fuskantar Zarge-Zargen Cin Hanci da Dukiyar da ba a San Asalinta baƳan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan Gaba
X whatsapp