Home SIYASA APC ta Mutu, Allah ya ji Kanta – Dino Melaye

APC ta Mutu, Allah ya ji Kanta – Dino Melaye

Lagos
Akinwunmi-Ambode lagos Governor

APC ta Mutu, Allah ya ji Kanta – Dino Melaye

 

A yanzu haka, rikicin shugabanci ya baibaye jam’iyyar APC gabannin babban taronta na kasa.

Sanata Dino Melaye ya yi amfani da wannan damar wajen yi mata ba’a, inda ya ce an yi juyin mulki a jam’iyyar mai mulki.

Ya kuma sanar a shafinsa na soshiyal midiya cewa APC ta mutu tare da yi mata addu’an samun rahama

Gabannin babban taron jam’iyyar All Progressives Congress (APC) wanda za a yi a ranar 26 ga watan Maris, sabon rikicin shugabanci ya kunno kai a jam’iyyar mai mulki.

Hakan ya biyo bayan darewa kujerar Gwamna Mai Mala Buni da Gwamna Sani Bello na jihar Neja ya yi a matsayin shugaban riko na jam’iyyar ta kasa, a ranar Litinin, 7 ga watan Maris.

Wannan ya sa Sanata Dino Melaye, tsohon dan majalisa da ya wakilci Kogi ta yamma a majalisar dattawa, yiwa jam’iyyar mai mulki ba’a.

An yi juyin mulki a APC – Dino Melaye

Dino ya je shafinsa na Instagram inda ya yi wani rubutu kan rikicin na APC sannan ya ce an yi juyin mulki a jam’iyyar mai mulki.

Ya ce: “Kwace ya kwace daga hannun wanda ya kwace….yepaaaaa. Juyin mulki a APC.”

APC ta mutu, Allah ya ji kanta

Dan siyasar bai tsaya a nan ba, ya kuma wallafa cewa APC ta mutu tare da yi mata addu’an Allah ya ji kanta.

Ya rubuta a shafin nasa:

“RIP APC: 2014 – 2022. Shekaru 8. Kin tafi da wuri haka. Mai sanarwa – SDM”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp