Home SIYASA Sunayen Sabbin Kwamishinonin Hukumar ICPC 5 da Majalissar Dattawa ta Tabbatar da...

Sunayen Sabbin Kwamishinonin Hukumar ICPC 5 da Majalissar Dattawa ta Tabbatar da su

Sunayen Sabbin Kwamishinonin Hukumar ICPC 5 da Majalissar Dattawa ta Tabbatar da su

 

Majalisar dattawa ta tabbatar da sabbin kwamishinonin hukumar ICPC biyar bayan shugaban kasa Buhari ya zabe su.

Majalisar ta tabbatar da kwamishinonin ne a zamanta na yau Laraba, 9 ga watan Maris.

Hakan ya biyo bayan samun rahoton kwamitin majalisar wanda ya tantancesu karkashin jagorancin Sanata Suleiman Abdu Kwari.

Abuja – Majalisar dattawa ta tabbatar da zababbun kwamishinonin hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC.

Majalisar ta tabbatar da su ne a ranar Laraba, 9 ga watan Maris, bayan duba rahoton kwamitin majalisar kan yaki da rashawa da laifukan da suka shafi kudi, jaridar Punch ta rahoto.

Sabbin kwamishinonin da aka tabbatar sun hada da:

1. Sanata Anthony Agbo

2. Anne Otelafu Odey

3. Alhaji Goni Ali Gujba

4. Dr. Louis Solomon Mandama

5. Olugbenga Adeyanju AIG (mai ritaya).

Buhari ya janye suna daya sannan ya maye gurbinsa da wani

A jawabinsa, shugaban kwamitin, Sanata Suleiman Abdu Kwari, ya tuna cewa shugaba Buhari ya janye sunan daya daga cikin zababbun kwamishinonin, Misis Mojisola Yaya-Kolade sannan ya maye gurbinta da Olugbenga Adeyanju AIG (mai ritaya), wanda kwamitin ya tantance.

Ya bayyana cewa zababbun kwamishinonin sun bayar da amsa yadda ya kamata yayin amsa tambayoyin kwamitin kan yadda za su cika aikin hukumar.

Ya kara da cewa, bayan bincikar takardunsu, kwamitin ya gamsu da cewa wadanda aka zaba suna da kwarewa, mutunci kuma za su iya sauke ayyukan da aka zabe su suyi.”

Ya kuma bayyana cewa, babu wani rahoto na tsaro ko korafe-korafe da aka yi kan wani daga cikin wadanda aka nada.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp