Home SIYASA Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

 

Tsohon gwamnan Borno da ke arewa maso gabas, Ali Modu Sheriff, ya ce ya janye daga takarar neman shugbancin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Modu Sheriff ya faɗa wa BBC Hausa cewa ya janye takarar ce saboda biyayya ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

“Shugaban ƙasa na son shugaban jam’iyya ya fito daga Arewa ta Tsakiya. Shugabanmu ne, babanmu ne, duk abin da yake so shi za mu yi. Ni ba na jayayya da iyayena a kowane fanni,” in ji shi.

Matakin tsohon gwamnan na zuwa ne bayan jam’iyyar ta ce ta ware wa shiyyar arewa ta tsakiya muƙamin shugaba na ƙasa yayin ganawar da gwamnoninta suka yi da Shugaba Buhari a watan Fabarairu.

An ware wa shiyyoyin Arewa muƙaman da na Kudu suka riƙe a cikin shekara takwas da suka wuce, su ma na Kudu haka, a cewar Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai.

Bisa wannan tsari ne jam’iyyar za ta zaɓi ssabbin shugabanninta a babban taron da za ta gudanar ranar 26 ga watan Maris.

‘Matakin da zan ɗauka nan gaba’

Ali Modu Sharif ya gode wa dukkan mutanen da suka goya masa baya”, amma ya ce ba zai daina siyasa ba.

“Ina jira daga nan zuwa Juma’a, idan jam’iyya ta ce kowane yanki zai iya tsayawa takara ina nan,” a cewarsa.

Da aka tambaye shi ko zai bar siyasa, sai ya amsa da cewa: “Ba zan bar siyasa ba. Don me zan bar siyasa?

“Ba zan nemi wani muƙami ba sai na shugaban jam’iyya saboda na taimaka wa jam’iyyarmu mai girma.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp