Home SIYASA 2023: Kudi na ke Bukata ba Kujerar Shugaban Kasa ba – Rotimi...

2023: Kudi na ke Bukata ba Kujerar Shugaban Kasa ba – Rotimi Amaechi ga Magoya Bayansa

2023: Kudi na ke Bukata ba Kujerar Shugaban Kasa ba – Rotimi Amaechi ga Magoya Bayansa

Rotimi Amaechi, Ministan Sufuri (Dan Amanar Daura) ya shaida wa magoya bayansa cewa shi fa yanzu kudi kawai ya ke bukata domin ya kula da kansa.

Ya yi wannan furucin ne yayin martani ga wasu kungiyoyin magoya bayansa da suka bukaci jam’iyyar mai mulki ta APC ta bashi tikitin takarar shugaban kasa a 2023.

Duk da hakan, wasu rahotanni sun nuna cewa an hangi fastocin takarar shugabancin kasa na Amaechi a wurin taron gangamin APC da aka yi a ranar Asabar.

Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, yayin da ya ke karyata jita-jitar cewa zai fito takarar shugaban kasa a 2023, ya bukaci magoya bayansa su bashi kudi a maimakon kujerar shugabancin kasar.

Idan za a tuna, The Punch ta rahoto cewa wata kungiya, Amaechi Vanguard a Amurka da Canada, ta bukaci jam’iyyar na APC ta zabi Amaechi a matsayin dan takarar jam’iyyar na shugaban kasa a 2023.

A bangarensa, Gwamna Nasir El-Rufai na Jihar Kaduna ya ce zai iya yin takarar shugabancin kasa a 2023 ne, a matsayin shugaban kasa ko mataimaki tare da Amaechi, idan Shugaba Buhari ya dage kan hakan.

Kudi na ke bukata ba kujerar shugaban kasa ba, Amaechi

Amaechi, yayin martaninsa game da bukatar ya fito takarar, ya ce abin da ya ke bukata kawai shine kudi da zai kula da kansa ba shugabancin kasa ba.

Da ya ke magana a Arise TV, ya ce:

“Mutanen da ke son in yi takarar shugabancin kasa a 2023, su bani kudi kawai. Ina bukatar kudi domin in kula da kai na.”

Amma, wasu rahotanni sun nuna cewa an ga hotunan takarar shugabancin kasa na Amaechi a wurare da dama a Eagles Square, inda aka yi taron gangamin jam’iyyar APC a ranar Asabar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp