‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 4 A Jihar Benue

Wani harin ‘Yan Bindiga yayi sanadiyyar halaka akalla mutun 4 a garin Ayilamo dake Karamar Hukumar Logo ta Jihar Benue.

Mazauna garin sun shaidawa PRNigeria cewa lamarin ya auku ne tsakar daren Talata yayin da al’ummar yankin ke tsaka da bacci.

Inda ‘Yan bindigar suka yiwa garin tsinke, tare da tsallakawa gidajen Al’umma inda suka harbe mutum 4 tare da barin wasu cikin muggana raunika.

Guda cikin shuwagabannin al’ummar garin, ya bayyana sunayen wadanda harin ya rutsa dasu da suka hadar da Vaachia Hangeior, Abako Kpeibee, Mtomga Akpi and David Akave.

Kawo lokacin kammala wannan rahoton kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar S.P Catherine Anene bata dauki kiran da muka yi mata ba, kuma bata bada amsar sakon karta kwana da muka tura mata ba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 15 minutes 55 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 57 minutes 20 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com