Home General ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 4 A Jihar Benue

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 4 A Jihar Benue

Wani harin ‘Yan Bindiga yayi sanadiyyar halaka akalla mutun 4 a garin Ayilamo dake Karamar Hukumar Logo ta Jihar Benue.

Mazauna garin sun shaidawa PRNigeria cewa lamarin ya auku ne tsakar daren Talata yayin da al’ummar yankin ke tsaka da bacci.

Inda ‘Yan bindigar suka yiwa garin tsinke, tare da tsallakawa gidajen Al’umma inda suka harbe mutum 4 tare da barin wasu cikin muggana raunika.

Guda cikin shuwagabannin al’ummar garin, ya bayyana sunayen wadanda harin ya rutsa dasu da suka hadar da Vaachia Hangeior, Abako Kpeibee, Mtomga Akpi and David Akave.

Kawo lokacin kammala wannan rahoton kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar S.P Catherine Anene bata dauki kiran da muka yi mata ba, kuma bata bada amsar sakon karta kwana da muka tura mata ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp