Home General ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 6 A Jihohin Kaduna Da Bauchi

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 6 A Jihohin Kaduna Da Bauchi

Wasu mabanbanta hare-hare sunyi sanadiyyar mutuwar mutum 6 a jihohin Kaduna da Bauchi.

PRNigeria ta ruwaito cewa maharani da ake zrgi ‘yan bindiga ne suna halaka wasu manoma a gonakin su a kauyen Iyatawa dake karamar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.

‘yan uwan wadanda lamarin ya rutsa dasu sunce mazauna kofar Jatau ne dake garin Zari’a, sun ce ‘yan  uwan nasu sun je gonakin nasu ne domin yin shuka, nan ne ‘yan bindigar suka haike musu, suka kuma halaka mutum 2 tare da yin garkuwa da  mutum 3.

Sun bayyana sunan wadanda ‘yan bindigar suka halaka da Alh. Mustapha lawan da Bello Lawal.

Sai dai an bayyana cewa ko a daminar Badi mahaifin wadanda aka halaka Alh. Lawal kofar Jatau ya tsallake rijiya da baya tare jin wasu muggana raunika a hannu ‘yan bindigar bayan da yaje gewaya gonar.

A wani labarin kuma wasu da ake zargin ‘yan bindiga sun kai hari garin Jamari Sabuwa dake  karamar hukumar Alkaleri ta jihar Bauchi, inda suka halaka mutum 4 tare da raunata mutum 3.

Shugaban karamar hukumar Alkaleri, Yusuf Garba, ya tabbatar da faruwar lamarin ranar Juma’a a garin Bauchi.

Yace ‘yan bindigar sun shiga garin ne inda sukayi garkuwa da Mai garin garin, bayan da Al’umma suka fahimci abinda ke faruwa ne suka tashi balli tare datarwatsa Shirin ‘yan bindiigar.

Shugaban karamar hukumarya tabbatar da cewa ‘yan bindigar sun fito daga cikin dajjin da yayi iyaka da jihohin Taraba, Gombe da kuma Plateau.

Wakilin mu ya rawaito mana cewa al’ummomin da lamarin ya shafa sun hadar da Tudun wada, Jada, Old Jamari, Sabuwa, Garin, Jauro Bano.

Wani mazaunin yankin Muhammad Usman ya shaidawa wakilin namu cewa ‘yan bindigar sun shiga garin ne da misalin karfe 11:45 na daren ranar Alhamis.

Kawo yanzu dai jami’an ‘yan sandan basu yi cikakken bayani kan wannan lamari ba, amma kakakin rundunar Muhammad Ahmad wakil yayi alkawarin tuntubar wakilin mu nan gaba kadan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp